Revelation of John 1

Gabatarwa

1Wahayin Yesu Kiristi, wanda Allah ya ba shi yǎ nuna wa bayinsa abin da lalle zai faru nan ba da daɗewa ba. Ya bayyana shi ta wurin aiko da malaʼikansa zuwa ga bawansa Yohanna, 2wanda ya shaida dukan abin da ya gani-wato, maganar Allah da kuma shaidar Yesu Kiristi. 3Mai albarka ne wanda yake karanta waɗannan kalmomin annabci, masu albarka ne kuma waɗanda suke jinsu, suke kuma sa abin da aka rubuta a ciki a zuciya, domin lokaci ya yi kusa.

Gaisuwa da Yabo

4Yohanna,

Zuwa ga ikkilisiyoyi bakwai da suke a lardin Asiya:

Alheri da salama gare ku daga shi wanda yake a yanzu, wanda yake a dā, da wanda zai zo, da kuma daga ruhohi bakwai da suke a gaban kursiyinsa,
5kuma daga Yesu Kiristi, wanda yake amintaccen shaida, ɗan farin daga tashin matattu, da kuma mai mulkin sarakunan duniya.

Gare shi wanda yake ƙaunarmu wanda kuma ya ʼyantar da mu daga zunubanmu ta wurin jininsa,
6ya kuma mai da mu masarauta da firistoci don mu yi wa Allahnsa da Ubansa hidima-a gare shi ɗaukaka da iko sun tabbata har abada abadin! Amin.

7Duba, yana zuwa cikin gizagizai,
kowane ido kuwa zai gan shi,
har da waɗanda suka soke shi;
dukan mutanen duniya kuwa za su yi makoki dominsa.
Bari yǎ zama haka nan! Amin.
8“Ni ne Alfa da kuma Omega,” in ji Ubangiji Allah, “wanda yake a yanzu, wanda yake a dā, da kuma wanda zai zo, Maɗaukaki.”

Wani Kama da Ɗan Mutum

9Ni, Yohanna, ɗanʼuwanku da kuma abokin tarayyarku cikin wahala da mulki, da kuma haƙurin jimrewa da suke namu cikin Yesu, ina can tsibirin Fatmos saboda maganar Allah da kuma saboda shaidar Yesu. 10A Ranar Ubangiji ina cikin Ruhu, sai na ji a bayana wata babbar murya kamar ƙaho, 11wadda ta ce: “Ka rubuta a cikin naɗaɗɗen littafi abin da ka gani ka kuma aika ta zuwa ga ikkilisiyoyi bakwai: zuwa Afisa, Simirna, Fergamum, Tiyatira, Sardis, Filadelfiya, da kuma Lawodiseya.”

12Sai na juya don in ga muryar da take magana da ni. Da na juya kuwa sai na ga alkukan fitilu bakwai na zinariya. 13A tsakiyar alkukan kuwa akwai wani “kama da ɗan mutum,”
Dan 7.13
saye da rigar da ya kai har ƙafafunsa da kuma ɗamarar zinariya ɗaure a ƙirjinsa.
14Kansa da kuma gashin fari ne fat kamar ulu, fari kamar dusar ƙanƙara, idanunsa kuwa kamar harshen wuta. 15Sawunsa sun yi kamar tagullar da take haske cikin matoya, muryarsa kuma ta yi kamar muryar ruwaye masu gudu. 16A hannunsa na dama ya riƙe taurari bakwai, daga bakinsa kuwa takobi mai kaifi biyu ya fito. Fuskarsa ta yi kamar rana mai haskakawa da dukan haskenta. 17Saʼad da na gan shi, sai na fāɗi a ƙafafunsa sai ka ce matacce. Sai ya ɗibiya hannunsa na dama a kaina ya ce: “Kada ka ji tsoro. Ni ne Farko da kuma Ƙarshe. 18Ni ne Rayayye, dā na mutu, ga shi kuwa ina a raye har abada abadin! Ina kuma riƙe da mabuɗan mutuwa da na Hades. 19Saboda haka, ka rubuta abin da ka gani, abin da yake yanzu, da abin da zai faru nan gaba. 20Asirin taurari bakwai da ka gani a hannuna na dama da kuma na alkukan fitilu bakwai na zinariya shi ne: Taurarin bakwai ɗin nan, malaʼikun ikkilisiyoyi bakwai ne; alkukan fitilu bakwai ɗin nan kuma ikkilisiyoyi bakwai ne.

Copyright information for HauSRK